
Daga Karshe Ali Nuhu Ya Janye Karar Da Yakewa Jarumar Kannywood Hannatu Bashir A Kotu
Daga Karshe Ali Nuhu Ya Janye Karar Da Yakewa Jarumar Kannywood Hannatu Bashir A Kotu
Bayan rigimar da ankayi tayi tsakanin jarumi ali Nuhu da jaruma Hannatu Bashir wanda abun har yakai ga zuwa kotu wanda abun ya samu asali ne akan aikin fim da hannatu Bashir keson ali Nuhu yayi mata amma hakan bai samu ba.
Shine tayi masa dogon rubutu ta haryae tura sako na kai tsaye wanda abun yaga kamar cin zarafi ne ali nuhu ya kaita kara to shine yanzu nan majiyarmu ta samu wani tattaurawa da rediyon freedom radio kano sunyi da lauyar ali nuhu inda take cewa.
“Sunana salima Muhammad sabo lauyar da ke kare Ali Nuhu daman an shigar da korafin ne domin tazo kotu ta gayyace ta, to last week bata zo ba saboda bata da lafiya.
To amma wannan sati an samu tazo an samu maslaha an samu anyi setting case din to na samu nayi withdrawal din wannan case tun Tuesday wanda kafin a shiga kotu ta sami Ali Nuhu ta bashi hakuri da ya janye wannan kara Ta samu wannan manya manya mutane a kannywood da manyan mutane da ke kano domin su bashi hakuri.
To shine kamar gobe za’a shiga kotu Ali Nuhu ya kirani yace ya janye karar kuma ya yafe mata duk abinda tayi masa.
Daga kashe lauyar tace alkali ya sanaanta su yace kada su sake wannan magana suje suci gaba da aiki tunda masana’antar su daya a kannywood industry”
Kalli Bidiyan Hirar Anan
Masu sauraranmu a Koda yaushe bayan Kun karanta wannan labarin zamu so karben a sahen mu na tsokaci.