Advertisement
Labaran Hausa
Trending

Wata Budurwa Kiristan Ta Bayyana Halaye Masu Kyau Da Ta Koya Daga Musulmai

Wata Budurwa Kiristan Ta Bayyana Halaye Masu Kyau Da Ta Koya Daga Musulmai

Wata budurwa mabiyar addinin kirista ta bayyana wasu muhimman dabi’u da ta koya daga wajen Musulmai.

A cikin wani bidiyo da budurwar mai suna Gayobi Achawa ta saka a shafin TikTok, ta bayyana cewa ita ba Musulma bace amma tana da ‘yan’uwa Musulmai a cikin danginta

Budurwar ta bayyana cewa wadannan halayen na Musulmai da ta koya wadanda suke matukar birgeta, ta koye su ne a wajen ‘yan’uwanta da kuma wajen yin aiki tare da Musulmai.

Ga jerin su kamar haka:

1. Mata Musulmai sun nuna mana cewa ba sai mace tayi shigar banza ba kafin kyawunta ya bayyana. Mata Musulmai za su rufe jikin su amma za ka ga kyawun su yayi matukar bayyana.

2. Biyayya, Musulmai nada matukar biyayya kan addinin su. Ba musulmin da zai bari a taba darajar Al-Qur’ani, manzon Allah (SAW) da Allah (SWT). Idan abota ta hadaku, to lallai komai rintsi komai wuya za su kasance tare da kai.

3. Musulmai ba munafukai bane, Musulmai ba ruwan su da munafurci idan suka ce za suyi abu to lallai gaskiyar kenan za suyi shi.

4. Yadda mata suke tsarkake jikin su bayan sun yi amfani da bandaki.

5. Kalmomi guda masu matukar muhimmanci wadanda suke min dadi a baki sune Insha Allah, Masha Allah da Alhamdulillah.

5. Kalmomi guda masu matukar muhimmanci wadanda suke min dadi a baki sune Insha Allah, Masha Allah da Alhamdulillah.

Kalli bidiyan yadda take Bayanin

Masu sauraranmu a Koda yaushe bayan Kun Kalli wannan bidiyan zamu so karben a sahen mu na tsokaci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button