Advertisement
Labaran Hausa

Yadda Aka Ceto Ran Wani Mutum Da Yayi Shekaru Ashrin A Kule A Wani Daki A Jihar Kaduna

Yadda Aka Ceto Ran Wani Mutum Da Yayi Shekaru Ashrin A Kule A Wani Daki A Jihar Kaduna

Yanzunan majiyarmu ta samu labarin yadda yan sanda suka ceto ran wani mutum da yayi shekaru ashrin a kule a wani daki kamar yadda shafin Bbc Hausa suka rawaito

Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta ƙaddamar da bincike kan dalilan da suka sanya aka kulle wani mutum a cikin ɗaki na tsawon shekara 20

A ranar Laraba ne ƴansandan suka ceto mutumin mai suna Ibrahim Ado, mai kimanin shekara 67 a wani yanki na birnin Kaduna da ake kira Bayajida

Mai magana da yawun rundunar ƴansanda a jihar Kaduna ASP Muhammed Jalige, ya ce jami’an rundunar sun kai samame a gidan da aka kulle mutumin ne bayan samun bayanan sirri

Ya ce mutumin mai kimanin shekara 67 ya kwashe tsawon shekarun ne yana garƙame a ɗakin, inda a nan yake cin abinci da kuma duk lamurransa.,, kuma an same shi cikin mummunan yanayi

Yanzu haka dai mutumin na samun kulawa a asibiti’

Masu sauraranmu a Koda yaushe bayan Kun karanta wannan labarin zamu so karben a sahen mu na tsokaci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button